Yayin da ake cigaba da samun bayanan da ke shigowa da tallafin kasashen waje dan yaudarar jama’a wadanda kuma su ke cigaba da kasancewa barazana ga daidaiton kasa, Cibiyar Samar da Sabbin Dabarun Aikin Jarida daTabbatar da Cigaba ko kuma CJID ta kaddamar da wani shirin da zai yi amfani da kafafen yada labarai wajen wayar da kan al’umma ta hanyar amfani da dabaru daban-daban wajen inganta zaman lafiya tsakanin al’ummomin da ke yankin arewacin Najeriya.
Wannan shirin wanda aka yi wa taken “Inganta yanayin juriya wajen amfani da yanar gizo-gizo da zaman lafiya a al’ummomi ta hanyar fadakarwa a kafafen yada labarai, karfafa tashoshin rediyo na gargajiya da yaki da yaduwar labaran karya,” na karkashin shirin tantance gaskiyar labaran cibiyar wato DUBAWA tare da hadin kan reshen da ke nazarin labaran karya ko wadanda ba daidai ba wadda aka fi sani da DAIDAC.
Shirin, wanda ke samun tallafin gwamnatin Kanada ta gidauniyarta mai tallafawa shirye-shiryen kananan al’ummomi (CFLI) na mayar da hankali ne wajen habaka gwamnatin da ke la’akari da kowa da kowa, da tsaro a jihohin Kano da Filato.
Jihohi daban-daban a yankin Arewacin Najeriya na fama da matsanancin talauci, rashin aikin yi tsakanin matasa, rashin ilimi, rashin jituwa tsakanin mabiya addinan da ke yankin kuma sun zama dandalolin habaka akidun karya wadanda ke samun goyon bayan kasashen waje.
Ire-iren wadannan bayanan yawanci sukan bulla ne a kafafen sadarwa irin su TikTok da Telegram, wadanda da ma an tsara su ne da nufin amfani da bambance-bambancen da ke tsakaninsu wajen haddasa rikici da kuma kaskantar da tsarin dimokiradiyya.
“Ba za mu iya yaki da yaduwar bayanan karya daga dakin labarai kadai ba,” Akintunde Babatunde, daretan cibiyar ya bayyana. “Al’ummomi ne ake fara haduwa da su wajwn wanzar da gaskiya. A wuraren ne labaran karya ke samun tushe, amma kuma wurare ne da za’a iya gina gaskiya.”
“Idan har muka nemi hadin kan jagororin addini, kungiyoyin matasa, da infuluwensas, mun dauki tattaunawar daga matakin manufofi zuwa matakin rayuwa irin ta yau da kullun, wanda zai taimakawa jama’a wajen ganin cewa tabbatar da inganci ko amincin bayanai ba alhakin da ya rataya a kan ‘yan jarida kadai ba, alhaki ne da ke kan kowa domin ya shafi dorewarta. Burinmu shi ne mu gina al’ummomin da za su iya gane karya a duk sadda suka ji ta su kuma kasance masu jimiri wadanda ba za su yadda a yaudare su da labaran karya ba,” ya bayyana.
Shirin wanda zai fara daga watan Nuwamban 2025, zai aiwatar da tsari ne wanda ke da bangarori daban-daban wajen gina ginshikin da zai tabbatar da irin juriyar da ake bukata daga kananan hukumomi zuwa sama. Mahimman abubuwan da za’a yi sun hada da samar da tashoshin rediyon al’ummomi da tarukan karawa juna sani na wayar da kan jama’a kan ire-iren abubuwan da ake yi a yanar gizo-gizo wa kungiyoyin matasa, shuwagabannin mata, jagororin al’umma da na addini, da shugabannin gargajiya a jijar tare da samar da kayayyakin da ke da tasiri a al’adun yankin wadanda za su tabbatar da cewa an yada bayanan kwarai a harsunan Hausa da Turanci.
Ta hanyar amfani da wannan shirin, cibiyar CJID za ta horas da jagororin al’umma, wakilan matasa, kungiyoyin mata, ma’aikata a kafafen yada labarai, da kungiyoyin fararen hula ta hanyar tattuanawa da su kan yadda labaran karya ke takurawa zaman lafiya da hadin kai da ma yadda al’ummomi za su iya gina kansu su jure idan har sun samu wayewa da sadarwa yadda ya kamata.
Sa hannu:
Akintunde Babatunde