Da’awa: Wani mai amfani da shafin Instagram na da’awar cewa Najeriya ta sanar da haramtawa ‘yan Amurka shiga kasarta a hukumance.

Hukunci: Karya ce. Sakamakon bincike ya nuna cewa babu wata kafar yada labarai mai nagarta da ta wallafa wannan labarin. Bugu da kari ma, ita kanta hukumar kula da shige da ficce ta NIS da gwamnatin Najeriya duk ba su fitar da wata sanarwar da ta bayyana hakan a hukumance ba.
Cikakken bayani
Ranar 22 ga watan Disemban 2025, Amurka ta fitar da kudurin shugaban kasa mai lamba 10998, wanda ya takaitawa baki shiga ya kuma dakatar da bayar da takardun izinin shiga kasar ta bisa ga kasashe 19 daga daya ga watan Janairun 2026.
Kasashen da wannan kudurin ya shafa sun hada da Angola, Antigua and Barbuda, Benin, Burundi, Côte d’Ivoire, Cuba, Dominica, Gabon, The Gambia, Malawi, Mauritania, Najeriya, Senegal, Tanzania, Togo, Tonga, Venezuela, Zambia, and Zimbabwe.
Kwanan nan wani mai amfani da shafin Instagram, headlines.360 ya yi da’awar cewa ita ma Najeriya ta fito a hukumance ta hana Amurkawa shiga kasarta abin da ya janyo wani rikicin diflomasiyya.
“Najeriya ta sanar a hukumance cewa ta haramtawa ‘yan Amurka shiga kasarta,” mai shafin na Instagram ya rubuta.
“Abun da ya kara ta’azzara damuwar da dama ake da shi a fuskar diflomasiyya da wasu karin tambayoyi dangane da tsaro, ramakon gayya da dangantakar da ke tsakanin Amurka da Afirka,” a cewar mai shafin.
A ranar Talata shida ga watan Janairun na 2026 mutane samda 1,400 sun sanya alamar like sa’annan yawan tsokacin da aka yo har ya gota 479.
Sauran masu amfani da shafin wadanda suka yi karo da labarin su ma sun yi tsokaci inda wadansun su suka yabawa gwamnatin Najeriya yayin da wasu kuma su ka nuna rashin yardar su.
“Labari mai kyau ‘yan Najeriya,” Lethibelas ya bayyana.
“Ya yi daidai,” in ji Seabornrena.
“Karya ce,” in ji Uyiexcellent wrote.
“Labaran bogi oh,” a cewar Kechamani.
Ganin yaddda aka sami ra’ayoyi mabanbanta ne ya sa DUBAWA tantance sahihancin labarin,
Tantancewa
DUBAWA ta fara da tantance mahimman kalmomi inda ta ga cewa babu wasu kafofi masu nagartan da suka wallafa labarin.
Daga nan mun duba shafin X na hukumar kula da shige da ficcen Najeriyar wato NIS dan ganin ko sun wallafa wani abu makamancin hakan amma ba mu ga komai ba.
Haka nan kuma mun duba shafin X na fadar shugaban kasa mu ga ko gwamnatin Najeriyar ce ta kaddamar da wannan sabuwar manufar wadda ta hana Amurkawa shiga Najeriyar amma nan ma ba mu ga komai dangane da wannan da’awar ba.
Ko da shi ke ma banda haka, ba mu ga wani martani daga fadar White House dangane da batun ba.
A Karshe
Bincike ya nuna cewa kafofin yada labarai masu nagarta ba su yi wannan labarin da mai amfani da shafin Instagram ya wallafa ba. Bacin haka ita ma hukmar kula da shige da ficce ba ta ce komai a kai ba. Haka ma ita kanta gwamnatin Najeriya. Dan haka wannan da’awar ba gaskiya ba ce.