Zargi: Wani mai amfani da tiwita na zargin wai ‘yan Boko Haram ne walkiya ta kashe yayin da suke hanyar zuwa Najeriya dan hallaka ‘yan kungiyar awaren Biafra
Zargin cewa walkiya ta kashe ‘yan Boko Haram yayin da su ke hanyar zuwa kashe ‘yan “Biafra” karya ne. Hoton da aka yi amfani da shi wajen zargin ba ma a Najeriya aka dauka ba. A Tanzaniya ne aka yi wannan gobarar a shekarar 2019
Cikakken bayani
Wani mai amfani da shafin Tiwita Dr Ken (@DrKen43273749) na zargin wai ‘yan kungiyar Boko Haram sun gamu da ajalin su yayin da su ke kokarin zuwa Najeriya dan kai hari kan ‘yan kungiyar awaren Biafra. Marubucin ya hada wannan labarin da wani hoto mai munin gaske wanda ke nuna gawawwakin mutanen da suka kone birjik a kasa mutane suna ziwa su kalla.
“Allahn kasar a kulluyaumin zai hallaka su. ‘Yan kungiyar Boko Haram yayn da suke kokarin shiga Najeriya su hallaka ‘yan Biafra amma walkiya ta fada a kansu ta yi sanadiyyar mutuwarsu” mai shafin ya bayyana.
Biafra da Boko Haram
Biafra jiha ce wadda masu ra’ayin raba Najeriya a yankin kudu maso gabashin kasar suka kirkiro bayan da wadansu shugabanin soji na kabilar Igbo suka yi gaban kansu suka bayyana cewa yankin ya sami ‘yancin kai daga Najeriya a shekarar 1967. Kasar ta kunchi yankin gabashin kasar inda mafi yawan mazauna yankin kabilar Igbo ne
Sai dai Biafra ta daina kasancewa kasa mai ‘yancin kai a watan Janairun 1970. Sai dai Kungiyar IPOB ta ‘yan asalin yankin Biafra ta bulla a shekarar 2012 a matsayin wata sabuwar kungiya a karkashin jagorancin Nnamdi Kanu da nufin farfado da ‘yantaciyar kasar ta Biafra.
Boko Haram ma sananniya ce Najeriya da ma kafafen yada labaran kasashen yamma inda nan ma an san ta da sunan “Boko Haram” wanda ke nufin “illimin boko ko karatu irin na kasashen yamma haramun ne.” Tun bayan kafuwar kungiyar a shekarar 2009, kungiyar ta haddasa tashin hankali a kasar inda ta yi sanadiyyar mutuwar mutane da dama a yayin da fararen hula da yawa kuma su ka rasa matsugunnensu, musamman a yankin arewa maso gabashin kasar.
Wannan zargin dai ya dauki hankali sosai a soshiyal mediya musamman a shafin Tiwita, inda su ke zargin wai makarakshiyar da Boko Haram ta kulla na kai hari a kan ‘yan kungiyar Biafra ya ci tura bayan da Allah ya aika da walkiya ta kona su a kan hanyarsu na kai harin.
Wani mai amfani da shafin, Taffy Ebuka (@taffyebuka) shi ma ya yi tsokaci yana cewa wai a baya ma an taba irin wannan yunkurin amma a wancan lokacin ma ya ci tura.
“Ko da yaushe yana faruwa da su a duk sadda su ka yi kokarin shiga kasar mu, a baya hatsari ne a wannan karon wuta Boko Fulani ba za ku yi nasara ba lokacinku ya kai 2023 lokacinmu ne.”
A halin da ake ciki yanzu Najeriya na fuskantar matsalolin tsaro kuma da labarai daban-daban masu sanya fargaba a zukatan jama’a irin wannan zargin zai iya kawao tashin hankali ko kuma ya sa mutane zama cikin wani yanayi na alhini.
Tantancewa
Da muka sanya hoton cikin manhajan binciken mafarin hotuna a google, sakamakon ya bayyana mana shafin Reddit a matsayin inda hoton ya fito cikin wani labarin da aka wallafa a shekarar 2019 dangane da fashewar wata tankar man da ta hallaka mutane fiye da 70.
Haka nan kuma an sake amfani da hoton a shafin Media Brest da Spy Uganda wadanda suka yi labarin cewa tankar man ta yi hatsari ne kafin ta kama da wutar da ta kashe mutane sama da 62 wadanda ke kokarin diban man da ke cikin tanakar bayan ta yi hatsarin a garin Morogoro da ke Tanzaniya.
A wani rahoton da CNN da ma wasu kafofin yada labarai sz ka yi sun tabbatar cewa lamarin ya afku ne a Tanzaniya. Hasali ma ‘yan sanda sun kwatanta hatsarin a matsayin mafi munin da aka taba gani a tarihin kasar da ke yankin gabashin Afirka.
Baya ga wadanda suka hallaka a wutar, gidan talbijin na kasar Tanzaniyar wato KBC ta ce alkaluman da ‘yan sanda su ka bayar na nuna cewa sama da mutane 70 ne su ka hallka a garin Mororgoro da ke da tazarar mil 120 daga yammacin cibiyar tattalin arzikin kasar wato Dar es Salaam.
Bugu da kari, a wani rahoton da jaridar Daily Express ta yi dangane da batun, ta yi amfani da wani hoton da ya nuna wani dan sanda yana tsaye a wurin da hatsarin ya afku. Wannan dan sandan ne ma ya sake bayyana a wannan hoton da ake zargin da shi abin da ya sake bayar da tabbacin cewa lamarin ya afku ne a Tanzaniya ba a Najeriya ba.
Ba wannan ba ne karon farko da DUBAWA ke karyata zargin da ya shafi wannan hatsarin da ya afku a aTanzaniya. Ko a watan Yunin wannan shekarar (2022) a WhastApp, an sake yada wani bidiyon da aka dauka lokacin da tankar ta kama da wuta ana zargin wai walkiya ta kashe ‘yan bindiga yayin da su ke hanyar zuwa Zamfara kashe kiristoci a jihar.
A Karshe
Hoton da ake amfani da shi ana yada labarin wai ‘yan Boko Haram sun kone yayin da su ke hanyar kai hari kan ‘yan Biafra da kuma yankin kudu maso gabashin kasar karya ne. A Tanzaniya ne aka dauki hoton lokacin da wata tankar mai ta kama da wuta ta hallaka wadanda ke kusa da ita
