Getting your Trinity Audio player ready...
|
Da’awa: Wani mai amfani da shafin Facebook ya yada wani bidiyo (video) da a cikinsa ake zargin tsohon gwamnan Kano Rabiu Musa Kwankwaso na kira da akai harin ramuwar gayya kan al’ummar Igbo da ke zaune a jihar Kano.

Hukunci: Yaudara ce! DUBAWA a bincike da ta gudanar ya nuna cewa Kwankwaso bai taba yin wani kira ba a kai farmaki kan al’ummar Igbo. Wannan bidiyo da aka yada a Facebook kwaskwarima ce aka yiwa wani tsohon bidiyon Kwankwaso da aka yada a a 2022.
Cikakken Sako
A ranar Alhamis 27 ga watan Maris, 2025 wasu mafarauta daga arewacin Najeriya ana zargin (alleged ) yi masu kisan gilla a wani gari mai suna Uromi a jihar Edo.
Lamarin ya jawo cece-ku-ce da kiraye-kiraye daga al’ummar da ke zaune a yanjin arewacin Najeriya, yayin da a bangare guda kuma aka kaddamar da kamfe na ganin an bi hakkin mutanen da aka kashe ta hanyar shari’a.
Ana tsaka da wannan ne sai ga wannan wallafa a Facebook. Mai amfani da shafin Dan Jarida, ya yada wani bidiyo inda tsohon gwamnan jihar ta Knao Rabiu Kwankwaso na alawadai da kisan gillar da aka yiwa mafarautan da ke kan hanyarsu ta komawa gida Kano daga jihar Rivers.
A sakonsa mai tsawon dakika 50 a bidiyon cikin harshen Hausa, Kwankwaso yayi kakkausan suka kan kisan matafiyan ‘yan arewa inda ya bukaci da a mayar da martani da ma neman ballewar arewaci daga Najeriyar.
“Ku “yankudancin Najeriya kuna kashe al’ummarmu ba tare da wani dalili ba, muna kai maku wake kuna kashe mu ku kona motocin, muna kai maku doya kuna kashe mu ku kona motocin, muna kai maku shanu da tumaki da akuyoyi, amma duk da haka kuna kashe mu, ba da dadewa ba ne aka sanar da ni cewa sun kashe direba da yaran mota sai suka watsar da gawarwakin kuma shiru kake ji, babu abin da aka yi, anan (arewacin Najeriya) shin muna zaune da ‘yankudanci lafiya? Tsohon gwamnan ya nuna bakin cikinsa , dole a ware ba za mu ci gaba da lamuntar wannan ba.”
DUBAWA ta nazarci yadda wannan wallafa ta dauki hankali da yadda ake ta martani. Ya zuwa ranar Laraba 2 ga watan Afrilu,2025 bidiyon ya samu martani 42,000 da wadanda suka kalla 1,000 da masu tsokaci 2,600 da wadanda suka sake wallafawa 5,600. Kasancewar akwai banbancin harshe ya zama abu mai wahala gano wasu bidiyo da ake hadawa da fasahar AI da wani harshe na cikin gida, mun samu wani bidiyon irinsa kamar anan here.
Mutane da dama kasancewar an yi bidiyon cikin harshen Hausa sun rika tsokaci kan bidiyon akasari sun yi amannar cewa wannan bidiyo na gaskiya ne, wasu na alakanta sautin muryar da Malamin nan Idris Abdulaziz Dutsen Tanshi.
Wani da ya nuna amannarsa, @ANasir Danmaliki ya rubuta, “Dan Musa Mai takalmin karfe GABA dai GABA dai jagora nagari,”
Haka shima Sufyan Abubakar yayi nasa tsokaci da cewa, “Mai girma Distinguish Sen. Rabi’u Musa Allah Ya ja zamaninka Allah yayima jagora,”
Shi kuwa anasa tsokaci, Abdullahi Sani yayi rubutun ne da cewa, “Wannan maganar Dr Idris Abdulaziz Dutsen Tanshi ce jagoran tirmishe shirka,”
Duba da irin martanin da ake yi kan wannan wallafa, DUBAWA ta shirya gudanar da bincike kan sahihancin bidiyon.
Tantancewa
Mun nazarci wannan bidiyo ta hanyar amfani da manhajar Yandex da manhajar gano asalin bidiyo ta Google Reverse Image Search. Sakamakon ya kai ga samun wani bidiyon irin wannan na Kwankwaso da aka yada a safin Facebook a shekarar 2022.
Da DUABAWA ta fassara wannan bidiyo sai ta bayyana cewa sakon barka da sallah ne ga al’ummar Musulmi a arewacin Najeriya inda yayi amfani da wannan dama wajen kira ga jama’a da su yi rijista da jam’iyyarsa ta NNPP gabanin zaben 2023.
DUBAWA ta yi kokari na gano banbanci da ke akwai tsakanin wannan bidiyo da wanda aka wallafa aka kuma yada a 2022, dukkaninsu an ga launin fari da kore a windo ko taga dake bayan Kwankwaso.
Hoto da aka dauka na Facebook daga asalin bidiyon, tushen hoto: Facebook
Na biyu babbar riga da Kwankwaso ya sanya da kujerar da yake zaune a kai dukkaninsu iri daya ne
DUBAWA har ila yau ta hanyar amfani da muhimman kalmomi a intanet ta bincika ko za ta samu wani rahoto da ake zargin tsohon gwamnan da wancan kalamai amma abin ya ci tura.
Ko da yake Kwankwaso yayi tsokaci (commented) kan kisan gillar na jihar Edo amma yayi ne a shafinsa na X a ranar 23 ga watan Maris, 2025, bayanansa babu inda ya nuna a raba kasa, Yayi ta’aziya ne ga iyalan mamatan da ma kira ga mahukunta da su gudanar da bincike cikin nutsuwa.
Jaridar Premium Times da Vanguard sun ba da rahoto inda tsohon gwamnan ya mika sakon ta’aziyarsa ga iyalan mamatan.
A Karshe
Da’awar karya ce, DUBAWA ta gano cewa bidiyon da aka wallafa a shafin Facebook an yada shi ne a can baya a 2022.