African LanguagesHausa

Da gaske ne! Akwai rahotanin da su ka tabbatar da cinikin kuri’u a Owo a zaben da ake yi a jihar Ondo

Getting your Trinity Audio player ready...

Bincike: Wani rahoton BBC Pidgin ya tabbatar da sahihancin bidiyon da aka dauka a adireshi mai lamda 016 ko kuma makarantar Ahmadiyya Grammar School, da ke Owo.

    Nazarin bidiyon da aka yi ta yin amfain da manhajar  INVID ya nuna cewa ba dadadewa ba aka sanya bidiyon cikin shafukan yanar gizo. An zantawar da aka yi da Fidelis David wani mai sanya ido daga jaridar TheCable ne ya tantance cewa harshen da aka yi amfani da shi wanda ake amfani da shi a Owo ne. Mr David wanda ya kasance a Owo tun da sassafe  ya ce duk da cewa shi bai ga musayar kudin da ake zargin an yi da idanunsa ba, ya lura cewa akwai wadanda sukan kada kuri’a sai su je gefe su nuna wa wasu wanda suka zaba kafin su jefa ta a cikin akwatin. Wata kila suna yin hakan ne saboda kudin da aka alkawarta musu.

    Haka nan kuma, shi ma Ayodele Oluwafemi, wani mai sanya ido daga  TheCable a karamar hukumar Kiribo Ese-Odo, ya fadawa NFC ya ce shi ma bai shaida karbar kudin da ido ba, amma ya ga wasu suna karbar wata ‘yar takarda wadda za su yi amfani da shi anjima su karbi abin da aka alkawarta musu.

    Da gaske ne! Akwai rahotanin da su ka tabbatar da cinikin kuri’u a Owo a zaben da ake yi a jihar Ondo

    Hukunci: Gaskiya ce

    Majiyoyi: Masu sanya ido,manhajar  INVID, BBC Pidgin

    Kwanan wata : 16/11/2024 

    Mawallafiya: Elizabeth Ogunbamowo

    EDITOCI: Ajibola Amzat, Simbiat Bakare, da Opeyemi Kehinde

    Show More

    Related Articles

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    Back to top button
    Translate »