Hoton X
|
Getting your Trinity Audio player ready...
|
Da’awa: Wani mai amfani da shafin X ya yada hoto inda yayi da’awar cewa ‘yansanda sun kama mambobi na kungiyar IPOB na safarar sassan jiki a jihar Imo.

Hukunci: Yaudara ce! Wannan hoto ya yadu a shafin intanet, tun a watan Agusta, 2021, kuma wannan bashi da alaka da kame-kamen da aka yi a baya-bayan nan bisa zargin masu safarar sassan jikin dan Adam.
Cikakken Sako
Sama da gawarwaki 100 ne aka gano sun fara rubewa an cire wasu sassa nasu a wani asibiti da hukuma bata yarda da shi ba karamar hukumar Ngor Ngor-Okpala a jihar Imo, wannan na zuwa bayan da ‘yansanda suka kai farmaki a asibitin da ke a jihar ta Imo , simamen da aka kai a ranar Asabar 6 ga Disamba,2025.
Wanda ke da mallakin wannan waje da aka bayyana da sunan Stanley Oparaugo, an gano yana gudanar da wani asibitin ajiyar gawarwaki mai zaman kansa tare da otel inda ake zarginsa da safarar sassan jikin dan Adam a fitar zuwa kasashen ketare cikin sirri.
Ana tsaka da wannan ne sai wani mai amfani da shafin X @fattylincorn, ya yada wani hoto inda yayi wata da’awa cewa ‘yansanda a Najeriya sun kama wasu mambobi na kungiyar nan mai fafutukar ganin an yi ware da samar da kasar Biafra wato (IPOB) inda kuma ya alakanta da gudanar da gidan ajiyar gawa wanda baya bisa ka’ida da ake gudanar da shi a jihar Imo.
Gama abin da yake cewa “Rundunar ‘yansanda ta kama mambobin IPOB bisa zargin gudanar da kasuwancin sassan jikin dan Adam a jihar Imo.”Wannan wallafa ta samu wadanda suka kalla sama da mutane 51,900 ya zuwa ranar Lahadi 15 ga watan Disamba,2025, wadanda suka nuna sha’awa (likes) 1,371 da wadanda suka sake wallafawa 550 da masu kafa hujja 39 da wadanda suke nuna cewa za su sake kalla (bookmarks) 71.
A bangare masu tsokaci kuwa an samu wadanda suka amince da wadanda suke nuna shakkunsu.
A cewar @LaudsamN IPOB masu aikata manyan laifuka ne, ba abokai ba, amma mun gode Allah an kama su.”
A nasa tsokaci @ThomasUthm98773 yace ne , “Al’ummar Ibo masu aikata manyan laifuka ne.”
Shi kuwa a nasa tsokaci @Truthonlykid yace ne “Ka nuna mana hujja cewa wannan abun ya faru ne a Imo ko kuwa mambobin IPOB ne.”
Mun kuma samu wasu wallafar da ita ma aka yada a Facebook kamar a nan da nan da nan.
Ganin cewa wannan abu ne da ake bukatar taka tsantsan, da yadda abun ya yadu kamar wutar daji DUBAWA ta ga dacewar gudanar da bincike kan wannan wallafa.
Tantancewa
DUBAWA da ta bi hanyar gano asalin hoto ta hanyar amfani da Google ta gano wannan hoto an yi amfani da shi a shafukan kafafan yada labarai da dama inda suka ba da labari yadda aka kama mambobi na IPOB ko hadakar masu tsaro ta ESN a watan Agusta,2021.
Jaridar Vanguard ta fitar da labari a ranar 2 ga watan Agusta,2021 inda ta ba da labarin kama mambobin IPOB da ESN 20 bisa zargin kashe-kashe da wasu miyagun laifuka a otel a karamar hukumar Orlu ta jihar Imo.
An kama kayayyaki da dama a hannun mambobin na ESN da aka kama tare da wasu mata bakwai a otel din cikin abubuwan kuma da aka kama har da kayan soja da kayan fada da harsashen bindiga da sauransu.
Haka ita ma jaridar TheNation, ta ba da rahoto irin wannan a 2021 inda tace Boniface Okeke wanda ya mallaki otel din da aka yi kamen ya bayyana cewa yana daukar nauyi tare da talafi ga IPOB/ESN inda ya basu kudade sama da miliyan ₦10 .
Suma wadannan jaridu Tribune da StreetJournal, da allAfrica suma sun ba da rahoto kan wannan batu a watan na Agusta,2021.
A Karshe
Binciken DUBAWA ya nunar da cewa hoton na da alaka da kai sumame maboyar ‘yantawayen na IPOB a jihar Imo a watan Agusta,2021 amma ba wai kamen da aka yi a wurin ajiyar gawa ba da ma yin kasuwanci na sassan jikin dan Adam.
