Sojan Najeriya yana kakkaɓo jirgi mara matuki (UAV). Haƙƙin mallaka: Military Africa.
|
Getting your Trinity Audio player ready...
|
Da’awa: Wani mai amfani da Facebook ya yi iƙirarin cewa wani jirgin yaki mara matuki na Iran ya bace hanya ya shigo Najeriya, inda sojojin Najeriya suka kakkabo shi a ƙauyen Dan Musa, Jihar Sokoto.

Hukunci: Ƙarya ce. DUBAWA ta gano cewa bidiyon ya samo asali ne daga ƙasar Iraki, ba Najeriya ba.
Cikakken bayani
Against this backdrop, a Facebook user shared a video (archived here) and alleged that an Iranian drone lost its way into Nigeria and was shot down by Nigerian troops in Dan Musa village, Sokoto State.
Yayin da rikici ke ƙara tsananta a yankin Gabas ta Tsakiya tsakanin Amurka, Isra’ila da Iran, rahotanni na nuna cewa ɓangarorin da abin ya shafa na amfani da jiragen yaki marasa matuƙa wajen kai hari da kuma sintiri.
A wannan yanayi ne wani mai amfani da Facebook ya wallafa wani bidiyo (an adana shi a nan) inda ya yi zargin cewa wani jirgin yaki mara matuki na Iran ya yi ɓatan hanya ya shigo Najeriya, kuma sojojin Najeriya suka kakkabo shi a ƙauyen Dan Musa, Jihar Sokoto.
Zuwa ranar Litinin, 2 ga Maris, 2025, bidiyon ya samu kallon mutane 30,200, martani 938, sharhi 422 da kuma rabawa sau 64.
Labarin ya haifar da muhawara iri-iri, inda wasu suka yi watsi da shi a matsayin abin da ba zai yiwu ba, yayin da wasu suka nuna sun amince da shi.
Another user, Auta Yaro, suggested the claim exposed contradictions in Nigeria’s security situation, implying that if troops could shoot down a foreign drone, they should be able to stop bandits operating in forests.
Saleem Muhammad Saraki ya mayar da martani cikin zolaya da cewa, “Kana nufin Najeriya za ta iya gano jiragen da ba nata ba? Madalla da Najeriya.”
Wani mai suna Auta Yaro kuwa ya ce wannan zargi yana nuna sabani a yanayin tsaron Najeriya, yana mai nuni da cewa idan har sojoji za su iya kakkabo jirgin wata ƙasa, to ya kamata su iya dakile ‘yan bindiga da ke kai hare-hare a dazuka.
Saboda yanayin siyasar duniya da zargin ya shafa da kuma yadda ya ja hankalin jama’a, DUBAWA ta yanke shawarar bincikensa.
Tantancewa
DUBAWA ta fara ne da duba bidiyon da kyau. Gajeren bidiyon ya nuna abin da ya yi kama da jirgin yaki mara matuki (UAV) da ya fadi a wani wuri mai ciyawa kore a yankin karkara. Sai dai, an gano sabani da dama a cikin bidiyon.
Sokoto na cikin yankin Sahel mai hamada. A watannin Fabrairu da Maris, yawancin filayen jihar sukan kasance busassu kuma ruwan kasa, ba su cika kasancewa da ciyawa kore mai yawa kamar yadda bidiyon ya nuna ba.

Hoton bidiyon da ke nuna ciyawa kore.
Zargin ya ambaci “ƙauyen Dan Musa, Jihar Sokoto”. Sai dai bincike ta Google ya nuna babu wani ƙauye da aka tabbatar da sunan Dan Musa a Jihar Sokoto.
Maimakon haka, Danmusa (wanda ake rubuta shi a wasu lokuta Dan Musa) ƙaramar hukuma ce a Jihar Katsina, ba a Sokoto ba. Wannan bambanci na wurin ya ƙara raunana sahihancin zargin.
Domin gano asalin bidiyon, DUBAWA ta yi amfani da Google Reverse Image Search ta hanyar amfani da hotunan bidiyon.
Sakamakon binciken ya nuna cewa Rudaw Türkçe, sashen harshen Turkiyya na Rudaw Media Network, wata kafar watsa labarai da ke Erbil, ta wallafa bidiyon a baya.
Kafar ta Turkiyya ta wallafa bidiyon a shafin X (wanda aka fi sani da Twitter) tare da rubutu da aka fassara kamar haka: “#VIDEO – Wani jirgin yaki mara matuki da aka ƙera a Iran ya fadi a ƙauyen Gırdaçal, wanda ke ƙarƙashin Erbil.”
Erbil birni ne a arewacin ƙasar Iraki, inda rahotanni suka tabbatar da hare-haren makamai masu linzami da jirage marasa matuƙa kan sansanonin sojojin Amurka daga wasu ƙungiyoyin mayakan Shi’a na Iraki masu goyon bayan Tehran.
Har ila yau, babu wata sanarwa daga Hedikwatar Tsaron Najeriya ko wata hukuma ta soja da ta tabbatar da cewa wani jirgin Iran ya shiga sararin samaniyar Najeriya ko kuma an kakkabo shi.
A Ƙarshe
Zargin cewa wani jirgin yaki mara matuki na Iran ya bace hanya ya shigo Najeriya kuma sojojin Najeriya suka kakkabo shi a ƙauyen Dan Musa, Jihar Sokoto, ƙarya ce.
